You are here: HomeAfricaBBC2023 05 23Article 1772402

BBC Hausa of Tuesday, 23 May 2023

    

Source: BBC

Ana tantama kan makomar Lopetegui a Wolves

Julen Lopetegui Julen Lopetegui

Ana tantama kan makomar kociyan Wolves, Julen Lopetegui, sakamakon yanayin tattalin arzikin kungiyar in ji dan jaridar Sifaniya, Guillem Balague.

Lopetegui, mai shekara 56, ya sanar a makon jiya cewar abu ne mai wahala kungiya ta taka rawar gani a Premier ba tare da jari mai tsoka ba.

Tsohon kociyan tawagar Sifaniya da Real Madrid ya ja ragamar Wolves za ta ci gaba da buga Premier a badi, bayan da kungiyar ta fuskanci barin gasar a bana.

Wolverhampton ta nada kociyan a cikin watan Nuwamba a lokacin da take kasa-kasan teburin babbar gasar tamaula ta Ingila ta bana.

Wolves ta zama ta hudu a Premier League, wadda take ta karshe teburi a Kirsimeti, amma ta samu gurbin ci gaba da buga gasar badi duk da saura wasa uku a kare kakar nan.

Ya ci wasa tara daga 22 da ya ja ragama a kakar nan, inda kungiyar tana ta 13 a teburi kafin a buga wasan karshe na bana.

Lopetegui ya ce shugaban kungiyar Jeff Shi, ya sanar da shi halin da ake ciki, wanda bai sani ba a baya.

Read full article