BBC Hausa of Tuesday, 12 July 2022
Source: BBC
A watan Agustan 2022 al'ummar ƙasar Kenya za su zabi sabon shugaban ƙasa.
Tuni ƴan takarar suka fara yaƙin neman zabe domin samun nasara.
A watan Mayun da ya gabata ma manyan ƴan takarar biyu suka zabi wadanda za su yi masu mataimaki.
Mataimakin shugaban kasar na yanzu da shi ma ke takara, ya zabi wani dan kasuwa Rigathi Gachagua yayin da tsohon firaminista Raila Odinga kuma ya zabi wata tsohuwar ministar shari'ar ƙasar Martha Karua.
Ga dai bayanai kan ƴan takarar da irin nasarorin da suka cimma a rayuwa: