You are here: HomeAfricaBBC2023 07 13Article 1803938

BBC Hausa of Thursday, 13 July 2023

    

Source: BBC

PSG ce kaɗai za ta iya sayen Osimhen - De Laurentiis

Victor Osimhen Victor Osimhen

Shugaban Napoli Aurelio De Laurentiis ya ce PSG ne kadai kulob guda daya kacal a duniya da ke da kuɗin da za ta iya ɓanɓare Victor Osimhen daga Stadio Diego Armando Maradona a bazaran nan.

Napoli ta yi sayo Osimhen mai shekaru 21 a shekara ta 2020 bayan dan Najeriyar ya shafe kaka daya kacal yana buga wa Lille a kan farashin yuro miliyan 70.

Amma kwalliya ta biya kuɗin sabulu, ganin Osimhen ya ci kwallaye 28 a kakar wasanni biyu na farko sannan ya ci 31 a karo na uku.

Kusan 26 daga cikin wadancan kwallayen sun zo ne a gasar Seria A yayin da Napoli ta samu Scudetto na farko cikin shekaru 33 da suka gabata.

Amma rawar da Osimhen ke takawa a Napoli ya jawo hankalin wasu manyan kungiyoyin kwallon kafa na turai, inda Chelsea da Manchester United da Real Madrid ke buƙatar sabon mai buga gaba.

De Laurentiis, wanda aka sani a duk faɗin duniyar ƙwallon ƙafa a matsayin mutum mai tsattsauran ra'ayi, ya dage a kan cewa Osimhen ba zai bar Napoli ba sai dai in ya sami wani gagarumin tayi kuma ya ce a halin yanzu PSG ne kadai ƙungiyar da ke da kwatankwacin kudin da ake bukata don sayen ɗan wasan.

Read full article