You are here: HomeAfricaBBC2021 08 25Article 1340788

BBC Hausa of Wednesday, 25 August 2021

    

Source: BBC

Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre ya rasu

Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre

Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre ya rasu ranar Talata yana da shekara 79, a cewar Ministan Shari'a na Senegal, Malick Sall.

Mista Habre ya rasu ne a asibiti yayin da yake zaman gidan yari a Senegal bisa aikata laifukan yaƙi a ƙasarsa da kuma lalata rayuwar 'yan Adam.

Wata kafar yaɗa labarai ta Senegal ta ce ya rasu ne sakamakon cutar korona, kamar yadda kamfanin labarai na AFP ya ruwaito.

A lokacin da ya mulki Chadi tsawon shekara takwas, shugaban ya dinga murƙushe 'yan adawa, abin da ya jawo mutuwar mutum fiye da 40,000, a cewar masu bincike.

A shekarar 2016 ne wata kotu ta musamman - wadda ƙungiyar haɗin kan Afirka (AU) da Senegal suka kafa - ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai.

An zargi Habre da aikata fyaɗe da bautarwa da kuma bayar da umarnin kisa a lokacin da yake kan mulki daga 1982 zuwa1990. Sai dai ya musanta zarge-zarge.

Wata hukumar bincike da aka kafa a Chadi bayan an kifar da gwamnatinsa a 1990 ta ce gwamnatin tasa ta aikata kisan da ke da alaƙa da siyasa 40,000 da kuma azabtar da mutum 200,000 cikin shekara takwas.

Read full article